Iran da Nijar sun sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar tsaro.

Iran da Nijar sun sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar tsaro.

Shugaban Rundunar Tsaron Iran, Janar Ahmad Rezaei Radan, ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami'an tsaro zuwa Jamhuriyar Nijar, inda suka gana da Ministan Cikin Gida na ƙasar, a wani mataki na ƙarfafa dangantakar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

A ganawar da aka gudanar, bangarorin biyu sun amince da kafa wani kwamitin kwararru da zai rika gudanar da tattaunawa akai-akai kan batutuwan da suka shafi tsaro da zaman lafiya a yankin.

Haka kuma, an sanya hannu kan wata yarjejeniya ta hadin gwiwa da ta kunshi muhimman fannoni kamar haka:

– Yaki da ta’addanci
– Hana laifukan ƙetare iyaka
– Yaki da safarar miyagun kwayoyi

Jami’an biyu sun bayyana aniyar ƙasashensu na aiki tare don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali, musamman a yankin Sahel da ke fama da matsalolin tsaro daban-daban

Creadt: Hoto: Nijar Hausa.

Post a Comment

0 Comments