Labaran Yau Lahadi 06/08/2023CE - 17/01/1445AH Ga Takaitattun Labaran Duniyar.

Labaran Yau  Lahadi 06/08/2023CE - 17/01/1445AH Ga Takaitattun Labaran Duniyar.







Majalisa ta ɗaga zaman tantance ministoci zuwa Litinin. 


'Yan majalisar Dattawa sun tilasta wa wanda za'a tantance a matsayin minista daga jihar Ogun Dr. Bosun Tijani neman afuwarsu da kuma 'yan kasa game da wasu kalamai da ya yi a shafukan sada zumunta a baya.


Yajin aiki: Likitocin Najeriya sun shirya gudanar da zanga-zanga a kowacce rana. 


An hallaka Mista Adeniyi Sanni, mai taimakawa Sanata Solomon Adeola a jihar Legas. 


Ganduje, ya ce surutan da mutanen Jihar Kano suka rika yi a kafafen sada zumunta kan nadin Maryam Shetty ne suka sa Shugaban Kasa ya canza shawararsa a kan nada ta minista.


Gwamnan Kano Abba K. Yusuf yace su na cigaba da bincike kan Abubakar Idris (Dadiyata) da ya bace a 2019.


Wani kasurgumin mai laifi da ake nema ruwa a jallo, Nasiru Abdullahi wanda aka fi sani da Chile Maidoki, ya mika wa hukuma kansa a Jihar Kano.


Bacewar gawar wata dattijuwa mai shekara 63 a yayin da ake shirin gudanar da jana’izarta a ranar Asabar ya haifar da rudani a Jihar Ondo.


Saudiyya ta umarci 'yan kasarta su fice daga Lebanon. 


MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar ayyukan jin kai a Jamhuriyar Congo. 


Shirin ECOWAS na tura sojoji Nijar yana tangal-tangal. 


Tsohon Firaministan Pakistan Imran Khan ya nemi magoya bayansa su yi zanga-zanga bayan kama. shi


Aljeriya da Majalisar dattawan Najeriya su ne na baya-bayan nan da suka ki amincewa a yi amfani da karfin soji kan dakarun da suka yi juyin mulki a Nijar yayin da wa'adin da ECOWAS ta ba su don mika mulki ke cika.


Brighton ta amince da yarjejeniyar da Mohammed Kudus, daga Ajax a kan kudi fam miliyan 34.5.


Arsenal za ta fafata da Man City a kofin Community Shield a yau Lahadi.

Post a Comment

0 Comments